Shin yaushe ne lokacin buda baki? (amsa)
Anonymous Apr 4, 02:39 PM

Shin yaushe ne lokacin buda baki? (amsa) 4

LOKACIN SHAN RUWA (BUƊA BAKI) : 𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓ : Assalamu Alaikum malam khamis Muna godiya sosai. Allah ya saka muku da alkhairi Ameen. Tambaya ta anan shine Yaushe ne lokacin buɗa baki (shan ruwa)? : 𝐀𝐌𝐒𝐀❗️ : Lokacin buɗa baki ya na tabbata ne da zarar rana ta faɗi. Dalili kuwa shine, hadisin da aka karbo daga Sahk ibn sa'ad, ya tabbata acikin Sahīhul Bukhārī daga Sahl Ibn Sa’ad yace: haqiqa Manzon Allah yace: Mutane ba zasu gushe tare da alheri ba matuqar suna gaggauta buɗa baki. Amma abin mamaki ayanzu sai kaga waɗansu mutane suna jinkirta buɗa baki har sai sunyi sallar magriba. Haqiqa yin haka ba qaramin kuskure bane, domin ya saɓawa koyarwar Manzon Allah ﷺ. Waɗansuma sai kaji su na cewa sai taurari sun bayyana, sannan suyi buɗa baki. Irin waɗannan mutane a tunanin su yin haka shine daidai, alhali kuwa ya saɓawa Sunnah, kamar yadda akayi bayani a hadisin daya gabata. Manzon Allahﷺ Yana cewa: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم ﺑﻜﺮﻭﺍ ﺑﺎﻹﻓﻄﺎﺭ ﻭ ﺃﺧﺮﻭﺍ ﺍﻟﺴﺤﻮﺭ ‏ [📕ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.(2835)] Manzon Allah (saw) Yãce: Ku Gaggauta Shan-ruwa, Kuma ku Jinkirta Sahur. قال رسول الله صلى الله عليه وسلم ﺛﻼﺙ ﻣﻦ ﺃﺧﻼﻕ ﺍﻟﻨﺒﻮﺓ: ﺗﻌﺠﻴﻞ ﺍﻹﻓﻄﺎﺭ، ﻭﺗﺄﺧﻴﺮﺍﻟﺴﺤﻮﺭ، ﻭﻭﺿﻊ ﺍﻟﻴﻤﻴﻦ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺸﻤﺎﻝ ﻓﻲ ﺍﻟﺼﻼﺓ [📗ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.(3038)] Manzon Allah (saw) Yãce: Abubuwa Uku Suna daga Cikin ɗabi'un Annabta, 1- Gaggauta Shan-ruwa, 2- Jinkirta Sahur, 3- 'Dora hannun dãma akan hagu a Sallah. Haka hadisin da aka karbo daga Abdullahi Ibn Abī Auf yace: "ya kasance tare da Manzon Allah ﷺ a lokacin tafiya suna azumi, sai rana ta faɗi, sai Manzon Allah ﷺ yace da wani daga cikin sahabbansa ya sauka ya shirya musu kayan buɗa baki sai, sahabin yace: "Ya Manzon Allah da sauran rana, akayi haka har sau uku, Manzon Allah ﷺ na cewa dashi ya shirya musu abin buɗa baki. Daga karshe bayan sun kammala sai Annabi yace: “Idan kuka ga dare ya gabato daga nan (wato rana ta faɗi), haqiqa mai azumi ya buɗe bakinsa (ana nufin koya sha ruwa ko bai sha ba) Bukhari da Muslim suka ruwaito shi. Daga Ansa bn Malik(RA) ya ce: Manzon Allah(ﷺ) ya kasance yana yin buɗe baki kafin ya yi sallah da danyen dabino, idan bai samu danyen dabino ba sai yayi da busassun dabino, idan kuma bai samu busasshen ba, sai ya kurɓi wasu kurɓi na ruwa". Tirmidhi ya ruwaitoshi ALLAH NE MAFI SANI
post

Replies

(0)

Related Posts


Trending

Are you ready!!! General
ina bukar taimako da shawara dan allah, porn ya lalata min rayuwa Lifestyle
i want PPA recommendation kano for my NYSC General
How and when ake ZAKKAN fidda kai? Religion
need more light on Abortion during ramadan Religion
A medical solution for those suffering from Addiction Health
(Inter tribal marriage) A Christian Yoruba lady marrying a Muslim Hausa man Marriage
✨🌙عيد مبارك General
Girlfriend dina da zan aura suddenly taji ta tsaneni Relationship
My relationship experience with a Christian girl Relationship
ku bani shawara please Advice
i am in difficult stuition my friends help me with advise Advice
I need advice on marrying a woman older than you. Relationship
how do i know if my boyfriend is not wasting my time Relationship