LOKACIN SHAN RUWA (BUƊA BAKI)
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Assalamu Alaikum malam khamis Muna godiya sosai. Allah ya saka muku da alkhairi Ameen. Tambaya ta anan shine Yaushe ne lokacin buɗa baki (shan ruwa)?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Lokacin buɗa baki ya na tabbata ne da zarar rana ta faɗi.
Dalili kuwa shine, hadisin da aka karbo daga Sahk ibn sa'ad, ya tabbata acikin Sahīhul Bukhārī daga Sahl Ibn Sa’ad yace: haqiqa Manzon Allah yace: Mutane ba zasu gushe tare da alheri ba matuqar suna gaggauta buɗa baki.
Amma abin mamaki ayanzu sai kaga waɗansu mutane suna jinkirta buɗa baki har sai sunyi sallar magriba.
Haqiqa yin haka ba qaramin kuskure bane, domin ya saɓawa koyarwar Manzon Allah ﷺ. Waɗansuma sai kaji su na cewa sai taurari sun bayyana, sannan suyi buɗa baki. Irin waɗannan mutane a tunanin su yin haka shine daidai, alhali kuwa ya saɓawa Sunnah, kamar yadda akayi bayani a hadisin daya gabata.
Manzon Allahﷺ Yana cewa:
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم
ﺑﻜﺮﻭﺍ ﺑﺎﻹﻓﻄﺎﺭ ﻭ ﺃﺧﺮﻭﺍ ﺍﻟﺴﺤﻮﺭ
[📕ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.(2835)]
Manzon Allah (saw) Yãce: Ku Gaggauta Shan-ruwa, Kuma ku Jinkirta Sahur.
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم
ﺛﻼﺙ ﻣﻦ ﺃﺧﻼﻕ ﺍﻟﻨﺒﻮﺓ: ﺗﻌﺠﻴﻞ ﺍﻹﻓﻄﺎﺭ، ﻭﺗﺄﺧﻴﺮﺍﻟﺴﺤﻮﺭ، ﻭﻭﺿﻊ ﺍﻟﻴﻤﻴﻦ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺸﻤﺎﻝ ﻓﻲ ﺍﻟﺼﻼﺓ
[📗ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.(3038)]
Manzon Allah (saw) Yãce: Abubuwa Uku Suna daga Cikin ɗabi'un Annabta,
1- Gaggauta Shan-ruwa,
2- Jinkirta Sahur,
3- 'Dora hannun dãma akan hagu a Sallah.
Haka hadisin da aka karbo daga Abdullahi Ibn Abī Auf yace: "ya kasance tare da Manzon Allah ﷺ a lokacin tafiya suna azumi, sai rana ta faɗi, sai Manzon Allah ﷺ yace da wani daga cikin sahabbansa ya sauka ya shirya musu kayan buɗa baki sai, sahabin yace: "Ya Manzon Allah da sauran rana, akayi haka har sau uku, Manzon Allah ﷺ na cewa dashi ya shirya musu abin buɗa baki. Daga karshe bayan sun kammala sai Annabi yace: “Idan kuka ga dare ya gabato daga nan (wato rana ta faɗi), haqiqa mai azumi ya buɗe bakinsa (ana nufin koya sha ruwa ko bai sha ba)
Bukhari da Muslim suka ruwaito shi.
Daga Ansa bn Malik(RA) ya ce: Manzon Allah(ﷺ) ya kasance yana yin buɗe baki kafin ya yi sallah da danyen dabino, idan bai samu danyen dabino ba sai yayi da busassun dabino, idan kuma bai samu busasshen ba, sai ya kurɓi wasu kurɓi na ruwa". Tirmidhi ya ruwaitoshi
ALLAH NE MAFI SANI
Related Posts
Trending Discussions
Wane course ne idan mutum yayi ze samu aiki
Yanzu, aiki se ahankali a kasar nan, wane course ko profession ne Wanda idan mutum yayi baze sha wah...
Read more
General
Family palava
It's still on the marriage issues let me share my experience, i came home from school some months ag...
Read more
General
what's bad in delaying marriage?
kawai dan mace ta kai certain age se a matsa mata ta kawo miji ni na kasa gane abin. like what's the...
Read more
Marriage
Addiction problem
I have porn addiction problem. Please I'm looking for someone who can help me out.
Advice
I need an advice about our relationship with my cousin
Malama I need your advice and yan aji abt our relationship with my cousin.. Muna soyayya dashi amma...
Read more
Relationship
My love for him ??? should I tell him?
Wallahi yanxu haha derris a guy Wanda nake mutuwan so??like am crushing on him for real.buh ya kasa...
Read more
Advice
Warning to others! How porn destroyed my life
I write this with a heavy heart, there is a new addictive substance out there it is Porn.
It all st...
Read more
Advice
I need Advice
So I'm new here please pardon my mistakes.
I used to have intense emotions towards my partners,the...
Read more
Advice
Join the Discussion
Sign in to share your thoughts and engage with the community.
Login to Comment