LOKACIN SHAN RUWA (BUƊA BAKI)
:
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
:
Assalamu Alaikum malam khamis Muna godiya sosai. Allah ya saka muku da alkhairi Ameen. Tambaya ta anan shine Yaushe ne lokacin buɗa baki (shan ruwa)?
:
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
:
Lokacin buɗa baki ya na tabbata ne da zarar rana ta faɗi.
Dalili kuwa shine, hadisin da aka karbo daga Sahk ibn sa'ad, ya tabbata acikin Sahīhul Bukhārī daga Sahl Ibn Sa’ad yace: haqiqa Manzon Allah yace: Mutane ba zasu gushe tare da alheri ba matuqar suna gaggauta buɗa baki.
Amma abin mamaki ayanzu sai kaga waɗansu mutane suna jinkirta buɗa baki har sai sunyi sallar magriba.
Haqiqa yin haka ba qaramin kuskure bane, domin ya saɓawa koyarwar Manzon Allah ﷺ. Waɗansuma sai kaji su na cewa sai taurari sun bayyana, sannan suyi buɗa baki. Irin waɗannan mutane a tunanin su yin haka shine daidai, alhali kuwa ya saɓawa Sunnah, kamar yadda akayi bayani a hadisin daya gabata.
Manzon Allahﷺ Yana cewa:
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم
ﺑﻜﺮﻭﺍ ﺑﺎﻹﻓﻄﺎﺭ ﻭ ﺃﺧﺮﻭﺍ ﺍﻟﺴﺤﻮﺭ
[📕ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.(2835)]
Manzon Allah (saw) Yãce: Ku Gaggauta Shan-ruwa, Kuma ku Jinkirta Sahur.
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم
ﺛﻼﺙ ﻣﻦ ﺃﺧﻼﻕ ﺍﻟﻨﺒﻮﺓ: ﺗﻌﺠﻴﻞ ﺍﻹﻓﻄﺎﺭ، ﻭﺗﺄﺧﻴﺮﺍﻟﺴﺤﻮﺭ، ﻭﻭﺿﻊ ﺍﻟﻴﻤﻴﻦ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺸﻤﺎﻝ ﻓﻲ ﺍﻟﺼﻼﺓ
[📗ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺠﺎﻣﻊ.(3038)]
Manzon Allah (saw) Yãce: Abubuwa Uku Suna daga Cikin ɗabi'un Annabta,
1- Gaggauta Shan-ruwa,
2- Jinkirta Sahur,
3- 'Dora hannun dãma akan hagu a Sallah.
Haka hadisin da aka karbo daga Abdullahi Ibn Abī Auf yace: "ya kasance tare da Manzon Allah ﷺ a lokacin tafiya suna azumi, sai rana ta faɗi, sai Manzon Allah ﷺ yace da wani daga cikin sahabbansa ya sauka ya shirya musu kayan buɗa baki sai, sahabin yace: "Ya Manzon Allah da sauran rana, akayi haka har sau uku, Manzon Allah ﷺ na cewa dashi ya shirya musu abin buɗa baki. Daga karshe bayan sun kammala sai Annabi yace: “Idan kuka ga dare ya gabato daga nan (wato rana ta faɗi), haqiqa mai azumi ya buɗe bakinsa (ana nufin koya sha ruwa ko bai sha ba)
Bukhari da Muslim suka ruwaito shi.
Daga Ansa bn Malik(RA) ya ce: Manzon Allah(ﷺ) ya kasance yana yin buɗe baki kafin ya yi sallah da danyen dabino, idan bai samu danyen dabino ba sai yayi da busassun dabino, idan kuma bai samu busasshen ba, sai ya kurɓi wasu kurɓi na ruwa". Tirmidhi ya ruwaitoshi
ALLAH NE MAFI SANI
Related Posts
Trending Discussions
Wane course ne idan mutum yayi ze samu aiki
Yanzu, aiki se ahankali a kasar nan, wane course ko profession ne Wanda idan mutum yayi baze sha wah...
Read more
General
how i feel about women
I wanted to share this to know if it is normal and some few men feel this way sometimes. i don't lik...
Read more
General
Miji na baya saduwa da ni? should i do this?
Miji na yayi aure tun April this year since then he doesn't even touch me sexually idan ma ya zo gid...
Read more
Marriage
unjust love
Assalamu alaykum people,, well lemme start from the very start, well I met this guy last year, Masha...
Read more
Advice
Should i do it? she's tempting me
I have a christian class mate that shows interest in me for the past 7 month. she looks good and has...
Read more
Advice
Why it's harder for ladies to get husbands.
Salam alaikum,
This topic was discussed on Instagram recently by Mr. Khaleeepha and some other brot...
Read more
Advice
Friend request
Good morning
I am yet to receive a request
I hope I have’nt done any mistakes during the registr...
Read more
Advice
Warning to others! How porn destroyed my life
I write this with a heavy heart, there is a new addictive substance out there it is Porn.
It all st...
Read more
Advice
What do ladies mean by "Financial stability" in men??
Can we get opinion of ladies on what they mean by man who's financial stable.
Is a hustler or self...
Read more
General
Join the Discussion
Sign in to share your thoughts and engage with the community.
Login to Comment