Gargadi Ga Alumar Hausawa
Nizam Aug 20, 03:46 PM

Gargadi Ga Alumar Hausawa 0

Wata sabuwar alada ce da ta shigo local hausa community da na lura, kuma naga yakamata a gargadi alumma. Watau iyaye na yin kuskure, wajen banbanta ga tarbiyar yara. Yarinya mace har tai aure sai ka ga itace islamiyya, itace, harda itace, boko, talla itace, in aike ya tashi a gida itace, ko kasuwa ne itace. ai ta rike ta gamgam ana dora ta kan hanya wai a karamin tunaninmu muna so ta kyautatta don ta samu miji nagari, kuma eh yarinya indai ba talla ake dora mata aba kokuma barinta ake zuwa yawo gidajen biki ba, eh sau dayawa ana saa… sai kaga yarinya ta tashi kamila da hankali kuma inshaa allahu in kai saa mai tsoron allah sai kaga alamarin abun shaawa. Duk wannan dai dai ne. Inda kuskuren yake shine wajen tarbiyan maza, santari wai sai kaga wai in yaro ya wuce jss 3 sai kaga iyaye sun fara sakan mai alamuransa. In ma yace bazai je boko sai a yardan mai. Balle kuma islamiyya baa Magana. Yanzu un kaje any islamiyya anan arewa alkawari sai kaga 80% duk matane, maza baa masu dole suje. Yo yaro bama ya yini gidansu baa san ina yake ba ina zaa kawo shi islamiyya, shidai amfanin shi lokacin damuna ya taya uban a gona. Daga nan ba ruwansa da mike faruwa gida. In ka tambaye shi ko iyayen sun tambaye shi sai yace ya fita dako kuma duk karya ce, kokuma kaji ance yana farauta kokuma kaji ance yana gidan dambe ko gidan gala ko gidan solo. Kokuma duk wani abu marar amfani. Shi da gida in yaji yunwa yazo gida yasha fate, ya ci tuwo. Kai abun kunya in ma yaro baya son fita yakai wani shekaru sai kaga wai koranshi akeyi ana cewa zam gida na mata ne yaje yai harka da abokansa. Duk iyaye na manta in yaro ya fita ko da kanshi kokuma in an korashi to fa zai fada chikin yan daba ne kokuma chikin yan shaye shaye, kokuma shikin yan fashi kokuma chikin yan kwace kan titi, abun dai baa kirgawa. Yaro bakasan harkokinshi, kila ma kana kwana da dan fashi, ko wani babban dan chacha ko dan daudu cikin gida bakasani. Gidajen hausawa ma da ake dakunan maza a waje baa san yaushe ya shigo ba ko ya fita koma in yak wan gida ba shin suma mazan ba yayanmu bane, namaji kadage kayi tarbiyar shi ma ya ka kare balle ka sake shi duniya. Abun da muka mantawa yarin yar nan da muke ta killace wa muna so ta samo miji na gari kashi 7 chikin 10 irin wannan yaron da ka sakar wa duniya fa irin shi fa zata jajibo tace tayi saurayi, ai masu aure. Shiya sa yanzu sai kaga yarinya masha allahu kana ta daukin wa zata kawo amma daga takawo mijin sai ka ganshi wani gaja, ko wani santolo , gashi gashi dai, bai chika mutumba ko a furucin shi. Kuma ba yanda zakai dole ka aura mata haka. Domin bakada wani wanda ya fishi da zaka kawo mata itama ta duba ta duba bata da wani wanda ya fishi… Yakamata alumma ta duba. Kada mu manta mu muka haifi yaran mu basu suka haifemu ba. Yanzu mutum in yaro ya gagare shi yace yabar mai gida sai kaji kowa yayi ca kanshi, yana chewa yai hakuri amma yaro sai ya zauna don ai gidan ubansa ne. kamar yanada wani permernent seat a gidan. Malamai a fadakar don Allah. Na gode
post

Replies

(14)
Abu-Bakr Aug 20, 05:04 PM
Wato na tuna lokacin dana cinye kudin makarantan islamiyana dana kannina na daina zuwa Da baba yagane na gudu yace shifa ya koreni agidanahi tunda islamiyane banaso da yunwa tayi maganina na kwana biyu haka na nimo tsofaffin anguwarmu da principal din islamiyar mu aka bashi hakuri ai saida nayi graduation Allah yasakawa iyayenmu da albarka amen
reply 1
Anonymous #2 Aug 20, 09:43 PM
Duk maganar ka gsk ne munyi rashin ji na gagara don Duk dukar da za kayi mun bazan Yi kuka bh, na Suma na farfado Amma with time da addua Allah ya shirye ni. 🤣🤣🤣 Boko kuwa tun littafan ss1 har ss3 Bnyi note ya Kai half na book din bh🤣 sai da na zamo ko Alaramman mu Bai kaii iya rubutun qurani na warash bh, shi da kan shi yke fadin haka. I was in the school since 2008 har ynxu Ina rubutun a allo Ina zuwa makaranta Kuma Ina final year a school na karantà electrical engineering. sai gashi ynxu wai wasu zasu ganni Kai har ynxu bka sauke bh, after all mu wadda muke karatu a tsangaya bama sauka see dai hawa
reply 1
Anonymous #1 Aug 23, 09:09 AM

Awwi 😂🤣
reply 0
Abu-Bakr Aug 23, 12:53 PM

Munsha duka fa
reply 0
Meenah2 Aug 27, 11:05 AM
well hw I wsh iyaye Mata zasuga saqon Nan su farka daga baccin da suke
reply 0
Anonymous #1 Aug 30, 01:44 AM

subhanallahi sannu
reply 0
Ahmad Aysha Sep 2, 12:29 AM

Ai Kawai Allah ya saka wa iyayen mu da gidanAljanna, ni fah da bulala ake rakani islamiyyah.
reply 0
Abu-Bakr Sep 2, 08:24 AM

amen amen aini ba bulala Amma innafita ba zuwa nakeba
reply 0
Ahmad Aysha Sep 2, 11:27 AM

Nima hakan nafara sai natafi gidan kawaye na ta wasa, so sai akafara tafiya daukata a makaranta sai malamina ya ce na kai 2 weeks bana zuwa, dana dawo ba wanda ya nuna min akan antafi nimana, akaban abinci naci harda pira sai da dare yayi aka dake ni😂😂 since from that day yayana yake rakani da bulala kuma ya sa malamina ya Dunga dukana if incase baya gari bai kawo ni bah kuma na missing.
reply 0
Abu-Bakr Sep 2, 11:33 AM

Omo kema kin taba kiriniya fa nidai naci kudin makarantan na Dana kannina yafi a irga ya Allah karka bamu Yara dazasuyi rashin jinda mukayi don wlh rashin ji ba dadi
reply 0

Related Posts


Trending

friendship Relationship
Why is it that working class guys like me only meet idle ladies Relationship
Dear girls, Relationship
Bare Ta Auri Dan Fulani General
What is your opinion on Jigida? General
Ya yanayin Sanyi a wajen ku at this time? General
Tambaya Entertainment
TEAM LEFE DOLE KO ASOKE LEFE Marriage
Why do men do this dan Allah? General
Guys on this app wan make me crazy Matchmaker
Your Birthday. Entertainment
Boredom General
A Message to My Princess (unknown wife) Marriage
Me yake fara zuwan ranka idan kayi tunanin Aure? Marriage